عربيEnglish

The Noble Qur'an Encyclopedia

Towards providing reliable exegeses and translations of the meanings of the Noble Qur'an in the world languages

The rising of the dead [Al-Qiyama] - Hausa language - Abu Bakr Jomy

Surah The rising of the dead [Al-Qiyama] Ayah 40 Location Maccah Number 75

Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin* kansa ba.

Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

Kada ka mõtsar* da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa* take.

To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?

Bai kasance ɗigo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;