Main pages

Surah The Opening [Al-Fatiha] in Hausa

Surah The Opening [Al-Fatiha] Ayah 7 Location Makkah Number 1

بِسۡمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحۡمَـٰنِ ٱلرَّحِیمِ ﴿1﴾

Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَـٰلَمِینَ ﴿2﴾

Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;

ٱلرَّحۡمَـٰنِ ٱلرَّحِیمِ ﴿3﴾

Mai rahama, Mai jin ƙai;

مَـٰلِكِ یَوۡمِ ٱلدِّینِ ﴿4﴾

Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.

إِیَّاكَ نَعۡبُدُ وَإِیَّاكَ نَسۡتَعِینُ ﴿5﴾

Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.

ٱهۡدِنَا ٱلصِّرَ ٰ⁠طَ ٱلۡمُسۡتَقِیمَ ﴿6﴾

Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.

صِرَ ٰ⁠طَ ٱلَّذِینَ أَنۡعَمۡتَ عَلَیۡهِمۡ غَیۡرِ ٱلۡمَغۡضُوبِ عَلَیۡهِمۡ وَلَا ٱلضَّاۤلِّینَ ﴿7﴾

Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.