Settings
Surah The Opening [Al-Fatiha] in Hausa
Surah The Opening [Al-Fatiha] Ayah 7 Location Makkah Number 1
بِسۡمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحۡمَـٰنِ ٱلرَّحِیمِ ﴿1﴾
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَـٰلَمِینَ ﴿2﴾
Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;
ٱلرَّحۡمَـٰنِ ٱلرَّحِیمِ ﴿3﴾
Mai rahama, Mai jin ƙai;
مَـٰلِكِ یَوۡمِ ٱلدِّینِ ﴿4﴾
Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.
إِیَّاكَ نَعۡبُدُ وَإِیَّاكَ نَسۡتَعِینُ ﴿5﴾
Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.
ٱهۡدِنَا ٱلصِّرَ ٰطَ ٱلۡمُسۡتَقِیمَ ﴿6﴾
Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.
صِرَ ٰطَ ٱلَّذِینَ أَنۡعَمۡتَ عَلَیۡهِمۡ غَیۡرِ ٱلۡمَغۡضُوبِ عَلَیۡهِمۡ وَلَا ٱلضَّاۤلِّینَ ﴿7﴾
Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.
English
Chinese
Spanish
Portuguese
Russian
Japanese
French
German
Italian
Hindi
Korean
Indonesian
Bengali
Albanian
Bosnian
Dutch
Malayalam
Romanian